Matthew 4:23-25
Yesu ya warkar da marasa lafiya
(Luka 6.17-19)
23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis, ▼▼Wato, Birane Goma
Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.
Copyright information for
HauSRK