Proverbs 29
1Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shiba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
2Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki
sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
3Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki,
amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
4Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo
amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
5Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki
yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
6Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa,
amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
7Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa,
amma mugaye ba su da wannan damuwa.
8Masu ba’a kan kuta faɗa a birni,
amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
9In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa,
wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
10Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci
su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
11Wawa yakan nuna fushinsa a fili,
amma mai hikima kan kanne fushinsa.
12In mai mulki yana sauraran ƙarairayi,
dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
13Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya.
Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
14In sarki yana hukunta talakawa da adalci
kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
15Sandar gyara kan ba da hikima,
amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
16Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa,
amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
17Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama;
zai ba ka farin cikin da kake so.
18Inda ba wahayi, mutane kan kangare;
amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
19Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai;
ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
20Ka ga mutum mai yin magana da garaje?
To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
21In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro,
zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
22Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa,
mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
23Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci
amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
24Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne;
yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
25Jin tsoron mutum tarko ne,
amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
26Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki,
amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
27Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya;
mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.
Copyright information for
HauSRK