Psalms 13
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. 1Har yaushe, ya Ubangiji? Za ka manta da ni har abada ne?Har yaushe za ka ɓoye fuskarka daga gare ni?
2Har yaushe zan yi kokawa da tunanina
kuma kowace rana in kasance da damuwa a zuciyata?
Har yaushe abokin gābana zai yi nasara a kaina?
3Ka dube ni ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna.
Ka ba da haske ga fuskata, ko in yi barci cikin mutuwa;
4abokin gābana zai ce, “Na sha ƙarfinsa,”
kuma abokan gābana za su yi murna sa’ad da na fāɗi.
5Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa;
zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
6Zan rera ga Ubangiji
gama ya yi mini alheri.
Copyright information for
HauSRK