‏ Psalms 136

1Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi.

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
2Ku yi godiya ga Allahn alloli.

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
3Ku yi godiya ga Ubangijin iyayengiji.

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

4Gare shi wanda shi kaɗai yake aikata abubuwan banmamaki,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
5Wanda ta wurin ganewarsa ya yi sammai,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
6Wanda ya shimfiɗa duniya a kan ruwaye,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
7Wanda ya yi manyan haskoki,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
8Rana don tă yi mulkin yini,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
9Wata da taurari kuma don su yi mulkin dare;

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

10Gare shi wanda ya kashe’ya’yan fari Masar

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
11Ya kuma fitar da Isra’ila daga cikinsu

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
12Da hannu mai ƙarfi da hannu mai iko;

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

13Gare shi wanda ya raba Jan Teku biyu

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
14Ya kawo Isra’ila ta tsakiyarsa,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
15Amma ya share Fir’auna da mayaƙansa cikin Jan Teku;

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

16Gare shi wanda ya bi da mutanensa cikin hamada,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

17Wanda ya buge manyan sarakuna,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
18Ya karkashe manyan sarakuna,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
19Sihon sarkin Amoriyawa

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
20Da kuma Og sarkin Bashan,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
21Ya kuma ba da ƙasarsu gādo,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
22Gādo ga bawansa Isra’ila;

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

23Shi wanda ya tuna da mu cikin ƙasƙancinmu

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
24Ya kuma’yantar da mu daga abokan gābanmu,

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
25Wanda kuma ke ba da abinci ga kowace halitta.

Ƙaunarsa madawwamiya ce.

26Ku yi godiya ga Allah na sama.

Ƙaunarsa madawwamiya ce.
Copyright information for HauSRK