‏ Psalms 23

Zabura ta Dawuda.

1Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
2Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa,
yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
3yakan maido da raina.
Yakan bi da ni a hanyoyin adalci
saboda sunansa.
4Ko da na yi tafiya
ta kwari na inuwar mutuwa,
Ko kuwa ta kwarin mafi duhu duka

ba zan ji tsoron mugu ba,
gama kana tare da ni;
bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya,
za su yi mini ta’aziyya.

5Ka shirya mini tebur
a gaban abokan gābana.
Ka shafe kaina da mai;
kwaf nawa ya cika har yana zuba.
6Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi
dukan kwanakin raina,
zan kuwa zauna a gidan Ubangiji
har abada.
Copyright information for HauSRK