‏ Luke 6:12-16

Manzanni sha biyu

(Mattiyu 10.1-4; Markus 3.13-19)

12Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah. 13Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.

14Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus,
Yaƙub,
Yohanna,
Filibus,
Bartolomeyu,
15Mattiyu,
Toma,
Yaƙub ɗan Alfayus,
Siman wanda ake kira Zilot,
16Yahuda ɗan Yaƙub,
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
Copyright information for HauSRK