‏ Mark 12:35-37

Kiristi ɗan wane ne?

(Mattiyu 22.41-46; Luka 20.41-44)

35Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne? 36Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
“Zauna a hannun damana
sai na sa abokan gābanka
a ƙarƙashin sawunka.” ’
Zab 110.1

37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?”

Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
Copyright information for HauSRK