‏ Matthew 10:1-4

Yesu ya aiki sha biyun

(Markus 3.13-19; Luka 6.12-16)

1Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.

2Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu,

da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus;
Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
3Filibus da Bartolomeyu;
Toma da Mattiyu mai karɓar haraji;
Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
4Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Copyright information for HauSRK